Daga Yusuf Aliyu Umar Gwammaja
Ƴansandan Najeriya a jihar Lagas da ke kudancin ƙasar sun kama wani direban mota ɗauke da bindigu da wasu makamai.
Kakakin rundunar Ƴansanda a jihar SP Benjamin Hundeyi, ne ya tabbatar da kama wanda ake zargin mai suna Azeez Babatunde, a ranar Alhamis ɗinnan.
“Da misalin karfe biyar na safiya ne, jami’an da ke yaƙi da aikata manayan laifuka na Ƴansanda, na ofishin Ƴansanda da ke Makodo,suka gano yadda direban ya yi juyowar gaggawa,zuwa titin Hakeem Dickson,wanda hakan tasa jami’an suka bi bayansa inda suka cafke shi”, in shi.
Ya kuma ce, jami’an rundunar sun kama wani mutum daya,da ya rage a cikin motar tare da direban motar, inda a yayin gudanar da bincike a motar aka gano ƙananan bindigun gami da bindigu kirar gargajiya da kuma wuƙa.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
An banka wa gidaje 24 da runbunan ajiyar hatsi wuta a jihar Jigawa bayan wani rikici ya ɓarke tsakanin Hausawa da Fulani.
-
Sojoji sun isa wasu ƙauyuka biyar a jihar Kebbi dan farwa Lakurawa, bayan sun kai harin da ya yi ajalin mutum 10.
-
Gwamantin Edo ta rushe gidan wani mutum saboda zarginsa da hannu a ayyukan garkuwa da mutane.
-
Gwamantin Kano ta ƙulla yarjejeniyar samar da sabbin motocin sufuri na zamani masu amfani da CNG.
-
Jam’iyyar PDP ta yi Alla wadai da dakatar da Sanata Natasha.