Tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari, ya koma gidan sa da ke Kaduna bayan ya kwashe kusan shekaru biyu a mahaifar sa Daura Jihar Katsina.
Buhari ya koma zuwa garin Daura tun bayan barin mulki a ranar 29 ga watan Mayu 2023.
Ɗaya daga cikin tsoffin hadiman sa a harkar yaɗa labarai Bashir Ahmad, shine ya bayyana hakan a shafin sada zumunta a ranar Alhamis, ya na mai cewa bayan kammala wa’adin mulkin sa na shekaru takwas, Buhari ya zabi rayuwa mai nutsuwa a garin su, inbda ya nisanci tattaunawar siyasa tare da mayar da hankali kan harkokin kansa.
Ya ce tsohon Shugaban ƙasar ya samu rakkiyar Mataimakin Shugaban Ƙasa Kashim Shettima, da manyan mutane ciki har da Gwamnan Jihar Borno Farfesa Babagana Zulum, da takwaran sa na Jihar Kaduna Uba Sani; da mataimakan gwamnan Jihar Katsina na yanzu da na baya, da tsohon Sufeto Janar na ‘Yan Sanda, da tsoffin ministoci, da wasu daga cikin hadiman sa na kusa.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Ƙudirin dokar da ke neman samar da Ofishin Firainista a matsayin Shugaban Gwamnati a Najeriya ya wuce karatu na 2 a majalisar wakilai.
-
Jami’an tsaro sun kama ɗalibai 59 a jihar Oyo
-
An dawo da ƴan Najeriya kusan 1000 gida daga ƙasar Libiya a farkon 2025 kawai
-
Masarautar Bauchi ta yi amai ta lashe kan soke hawan Sallah.
-
Kwastam ta kwace kuɗi kimanin naira biliyan 289 da aka boyi a katon ɗin yoghurt a Filin Jirgin Saman Abuja