Daga Suleman Ibrahim Modibbo
rahotanni a Najeriya sun ce a jiya ne tsohon gwamnan babban bankin Najeriya, CBN, Godwin Emefiele, ya isa gidansa da ke Abuja, bayan da wata babbar kotun Abuja ta bayar da belinsa.
BBC ta ce Emefiele ya shafe “kwanaki 151 a hannun jami’an tsaro”.
Babbar kotun tarayyar Najeriya da ke zamanta a Maitama ta bayar da umarnin a sake shi daga gidan yari, duk da rashin amincewar da babban lauyan gwamnatin tarayya, AGF, da hukumar yaki da cin-hanci da rashawa EFCC suka yi.
Babu Wanda Zai Daina Karɓar Kuɗaɗen Naira Da CBN Ya Samar- Babban Bankin Najeriya.
Kotun, a hukuncin da mai shari’a Olukayode Adeniyi ya yanke, ta bayar da umarnin a saki tsohon gwamnan babban bankin ga lauyoyinsa, duk da cewa ta umarce shi da ya miƙa dukkan takardun tafiye-tafiyen sa na kasashen waje.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
An banka wa gidaje 24 da runbunan ajiyar hatsi wuta a jihar Jigawa bayan wani rikici ya ɓarke tsakanin Hausawa da Fulani.
-
Sojoji sun isa wasu ƙauyuka biyar a jihar Kebbi dan farwa Lakurawa, bayan sun kai harin da ya yi ajalin mutum 10.
-
Gwamantin Edo ta rushe gidan wani mutum saboda zarginsa da hannu a ayyukan garkuwa da mutane.
-
Gwamantin Kano ta ƙulla yarjejeniyar samar da sabbin motocin sufuri na zamani masu amfani da CNG.
-
Jam’iyyar PDP ta yi Alla wadai da dakatar da Sanata Natasha.