October 16, 2024

Warning: sprintf(): Too few arguments in /home/martabaf/public_html/wp-content/themes/elegant-magazine/lib/breadcrumbs/breadcrumbs.php on line 254

A Yau Asabar Ne Ake Zaɓen Ƙananan Hukumomin Jihar Jigawa.

Wasu rahotanni daga jihar Jigawa na nuni da cewa, an samu ƙarancin mutane da za su kaɗa ƙuri’a a zaɓen ƙananan hukumomi da ke gudana a yau Asabar a jihar Jigawa.

Daily Trust ta lura cewa yayin da jami’an tsaro da na zaɓe su ka kasance a wasu rumfunan zaɓe, an bar su da jiran kayan zaɓen domin har zuwa wasu awanni al’umma ba su fito kada kuri’a ba.

A cewar Trust, haka abin yake a mazabar Jigawar Tsada, inda ma’aikatan zabe ke zaune tsuru-tsuru su na tsimayen masu zaɓe.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *