Daga Suleman Ibrahim Modibbo
Wata amarya mai suna Khadija Abdullahi, a unguwar Kwajalawa da ke birnin Kano ta rasa warin idonta daya a lokacin da ake tsakiyar bikinta ana gobe daurin aure.
Rundunar yan sandan jihar ta tabbatar da afkuwar lamarin ta bakin Kakinta Sifiritandan Yan Sanda Abdullahi Haruna Kiyawa, inda ya ce tini sun kama mutum biyu da ake zargi da aikata laifin.
Wanda ya ce kama mutum biyun ya biyo bayan korafi da amaryar Khadija ta shigar ga yan sanda ne tin a ranar 13 ga watan Junairu na shekarar 2023 da muke ciki “ ta shigar da karafi a ofishin yan sanda na Zango a kan cewa suna bikin aurenta sun kunna kidan DJ a kofar gida, wadansu yan Vigilanty su zo suka ce lallai fa sai an dena, sun hana wannan kidan DJ a unguwa, ta dalilin haka ne tana tasaye sai taji jifa a idonta,” in ji shi.
Kiyawa, ya kuma ce, an dauketa an kai ta asibiti inda likita ya tabbatar da cewa ta samu raunuka sama da kuma kasan idanun nata.
“Yanzu haka dai mun kama mutane biyu Yahaya da kuma salisu alhajin kwari da tini an gurfanar da su a gaban kotu, a cewarsa.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Kotu Ta Daure Wani Matashi Watanni 15 Kan Shiga Gidan Tsohon Gwamnan Jihar Bauchi M.A.
-
Zargin Taimakawa Ta’addanci: SSS Sun Mamaye Hedikwatar Babban Bankin Najeriya.
-
Gwamna Bala ya sha alwashin inganta tsaro, yaƙi da talauci, yayi yaƙin neman zaɓe a Itas
-
Ciyar Da Jihar Bauchi Gaba Ne Muradin Mu, Ku Sake Ba Mu Dama – Saƙon Gwamna Bala Ga Al’umar Udubo
-
Ƴan siyasa ku guji amfani da mimbarin Wa’azi domin biyan bukatar ku – Abdulkarim Tilde