Daga Suleman Ibrahim Modibbo
Wasu rahotanni da ke fitowa daga jihar Borno na cewa, al’umma mazaunin birnin Maiduguri sun shafe daren jiya ba tare da bacci ba, saboda mummunar bala’in Ambaliyar Ruwa da ta mamaye birnin.
Jama’a da dama ne suka taru a kofar fadar Shehun Borno, in da suke neman mafaka, ko da dai nan ɗin ma ruwa ya mamaye wani bangare.
Tini dai hukumar kashe Gobara da sauran hukumomi suka dukufa wajen shawo kan matsalar, in ake kai agajin gaggawa ga waɗanda bala’in ya shafa.
Daman Gwamnatin jihar ta yi ta wayar da kai mutane kan hasashen samun Ambaliyar Ruwan, in da Gwamna Umar Zulum ya bayar da umarni rufe makarantun Firamare da Sakandare a jihar domin kare yara daga barazanar Ambaliyar.
Hukumomi a Najeriya sun yi hasashen samun Ambaliyar Ruwa a wasu jihohin Najeriya 21 sakamakon ruwan da za a yi ta yi tsawon kwanaki ba tare da ƙaƙƙautawa ba.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Gwamnatin Kano ta tabbatar da za ta yi adalci da sauraron ƙorafe-ƙorafen al’ummar da aikin magance zai zayar ƙasa zai shafa a Bulbula tare da biyan diyya
-
Buba Galadima ya ƙaryata batun komawar Kwankwaso APC da Ganduje ya yi
-
NSCDC ta tura Jami’ai 415 a Zamfara don tabbatar da tsaro lokacin bukukuwan Easter
-
Ƴansandan Najeriya Najeriya sun cafke mutum biyu kan rikicin baya-bayan nan da ya afku a jihar Filato
-
Shugaba Tinubu ya ƙaddamar da sabon kwamitin ƙidaya