Daga Suleman Ibrahim Modibbo
Wasu bayanai da ke fitowa daga birnin Kano na cewa Hukumar Karɓar korafe-korafe ta Jihar Kano, ta gano wani babban rumbun ajiya da ake sauyawa shinkafar tallafi ta Gwamnatin Tarayya buhu domin sayarwa.
Hikima Radio ta rawaito cewa an gano shinkafar ne a unguwar Hotoro da ke birnin Kano.
Gwamnan Abba ya zargi gwamnatin Ganduje da cin hanci da rashawa da gazawa wajen tsara birane.
Shinkafar wanda yawanta ya kai Tirela 23 na ɗauke da hoton Shugaba Bola Ahmad Tinubu wanda aka rubutu cewa shinkafar ba ta sayarwa ba ce.
A baya dai shugaba Tinubu ya aiko da shinkafa jihar Kano a wani mataki na rage wa al’umma raɗaɗin halin da suke ciki na matsin rayuwa.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Masu garkuwa da mutane sun nemi kuɗin fansa na Naira miliyan 100 domin sakin Fasto a jihar Kaduna.
-
Jami’an tsaro a Zamfara sun ƙaddamar da farautar Ƴanbindiga a wani yankin jihar bayan sun yi ajalin mutum biyu tare da sace wasu 26.
-
Gwamnatin Cross River ta gargadi shugabannin ƙananan hukumomin jihar kan biyan albashin malaman makaranta.
-
Babban Bankin Najeriya ya samun ƙarin kuɗaɗen shiga da ya kai dala biliyan 6.83 a shekarar 2024.
-
Peter Obi ya gode wa Ƴansanda kan janye gayyatar da su ka yi wa Sarki Sunusi.