Wata babbar kotun jihar Jigawa da ke zama a Dutse karkashin jagorancin Mai shari’a Muhammad Abubakar Sambo ta yanke wa Isah Haruna hukuncin ɗaurin rai-da-rai bayan samunsa da laifin yin luwaɗi.
An gurfanar da wanda ake tuhumar ne ranar 2 ga watan Mayun 2023, bisa zargin aikata fyaɗe, lamarin da ya saɓa wa sashe na 3 na dokar hana cin zarafin lalata ta (VAPP) a jihar Jigawa 2021.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa a ranar 10 ga watan Yunin 2022, wanda aka yanke wa hukuncin ya yaudari wani yaro ɗan shekara 14 a wani kanti da ke Gwaram Sabuwa, a karamar hukumar Gwaram a jihar Jigawa, inda ya yi luwaɗi da shi.
Lauyan mai shigar da ƙara, Sunusi Sani, ya gabatar da shaidu biyar a kan wanda ake kara, shi kuma wanda ake kara ya bayar da shaida don kare kansa.
Alkali mai yanke hukunci, ya bayyana cewa masu gabatar da ƙara sun gabatar da dukkan hujjoji da suka nuna cewa wanda ake ƙara ya aikata luwaɗi, inda ya yanke wa Isa Haruna hukuncin ɗaurin rai-da-rai.
A wani hukunci kuma, babbar kotu mai lamba 6 da ke zamanta a Birnin Kudu a karkashin Mai shari’a Musa Ubale, ta samu wani Ibrahim Sani da ke kauyen Kiyako na karamar hukumar Birnin Kudu da laifin luwadi da yara, inda ta yanke masa hukuncin ɗaurin rai-da-rai.
An gurfanar da wanda ake tuhumar ne a gaban kotu, bisa tuhuma shida da suka haɗa da luwadi.
Ana zarginsa da yin luwaɗi da wasu yara maza shida masu shekaru tsakanin 11 zuwa 16, laifin kuma da ya saɓa wa sashe na 284 (1) na kundin laifuka wanda aka yi wa gyara na 2014.
BBC Hausa
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
An banka wa gidaje 24 da runbunan ajiyar hatsi wuta a jihar Jigawa bayan wani rikici ya ɓarke tsakanin Hausawa da Fulani.
-
Sojoji sun isa wasu ƙauyuka biyar a jihar Kebbi dan farwa Lakurawa, bayan sun kai harin da ya yi ajalin mutum 10.
-
Gwamantin Edo ta rushe gidan wani mutum saboda zarginsa da hannu a ayyukan garkuwa da mutane.
-
Gwamantin Kano ta ƙulla yarjejeniyar samar da sabbin motocin sufuri na zamani masu amfani da CNG.
-
Jam’iyyar PDP ta yi Alla wadai da dakatar da Sanata Natasha.