June 8, 2023

Warning: sprintf(): Too few arguments in /home/martabaf/public_html/wp-content/themes/elegant-magazine/lib/breadcrumbs/breadcrumbs.php on line 254

APC Ta Cinye Zaɓen Gwamna A Jihar Jigawa.

Page Visited: 94
0 0
Read Time:38 Second

Daga Suleman Ibrahim Modibbo

Hukumar zaɓen Najeriya INEC ta sanar da mataimakin gwamnan jihar Jigawa kuma ɗan takarar gwamnan jihar a jam’iyyar APC mai mulki, Alhaji Umar Namadi a matsayin wanda ya lashe zaɓen gwamnan jihar da ya gudana a ranar Asabar.

BBC Hausa ta rawaito cewa Namadi ya lashe zabe a ƙananan hukumomi 26 daga cikin 27 na jihar.

Ya samu kuri’u 618,449 inda ya samu galaba a kan ‘yan takarar jam’iyyar PDP, Mustapha Sule Lamido da kuma NNPP Aminu Ibrahim wanda ya zo na uku.

Dan takarar PDP ya samu kuri’u 368,726 a yayin da ɗan takarar NNPP ya samu ƙuri’u 37,156.

Babban jami’in da ke kula da zaben, Farfesa Zaiyanu Umar ne ya sanar da sakamakon zaben a ranar Lahadi.

Average Rating

5 Star
0%
4 Star
0%
3 Star
0%
2 Star
0%
1 Star
0%

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *