Daga Suleman Ibrahim Modibbo
Jam’iyyar APC a jihar Kano, ta bukaci hukumar EFCC, da ta kaddamar da bincike kan abin da ta kira “badaƙala” ta baya-bayan nan da ta shafi kashe kuɗaɗen da ake zargin na kwangilar samar da magunguna ga kananan hukumomi 44 na jihar.
Hakan ya biyo bayan bidiyon da Ɗan Bello ya saki ne, wanda ake zargin ana yin abin da bai dace ba wajen siyen magunguna a ƙananan hukumomin, tare da kefe wani kamfani ana bashi kwangilar.
Tini dai gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf, ya bayar da umarni a yi bincike kan lamarin ya na mai cewa bashi da masaniya kan batun.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
PDP ta sake dage taron Kwamitin Zartaswar ta na Kasa (NEC) zuwa ranar 15 ga watan Mayu.
-
Mijin Sanata Matasha ya buƙaci Akpabio da ya girmama matar sa.
-
Tinubu ya ya tabbatar da cewa tattalin arziƙin Najeriya ya na farfaɗo wa.
-
Ba zan yi musayar yawu da El-Rufai ba,-Ribadu
-
“Dubban mutane na shigowa jam’iyyar mu, ba da daɗewa ba, za mu karɓi manyan jiga-jigan NNPP da kansu”-Ganduje