April 1, 2025

Warning: sprintf(): Too few arguments in /home/martabaf/public_html/wp-content/themes/elegant-magazine/lib/breadcrumbs/breadcrumbs.php on line 254

Atiku ya buƙaci gwamnatin Najeriya ta yi bincike kan zargin lalata da na Natasha ta yi wa shugaban majalisar Dattawa Godswill Akpabio.

Tsohon Mataimakin Shugaban Kasa Atiku Abubakar, ya nuna damuwa kan zargin cin zarafi, tsoratarwa, da rashin adalci da aka yi wa Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, wanda Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta gabatar, ya bukaci a gudanar da “bincike mai zurfi, cikin adalci, kuma na gaskiya.”

A wani saƙo da ya wallafa a shafin sa na X, Atiku ya buƙaci Shugaba Bola Tinubu da Majalisar Dattawa da su ɗauki waɗannan zarge-zarge da muhimmanci ta hanyar tabbatar da “bincike na kwarai, na gaskiya.

Atiku ya ce, “Tunda yanzu akwai mata huɗu kacal a Majalisar Dattawa, dole ne mu samar da yanayi da zai ba su damar yin aiki ba tare da tsoro ko cin zarafi ba.”

“Wannan lokaci ana buƙatar ɗaukar mataki mai hikima da adalci domin kare mutuncin hukumomin mu da tabbatar da cewa kowane dan Najeriya ba tare da la’akari da jinsi ba, ya na samun mutunci da girmamawa.”

A cewar jagoran adawa, “waɗannan zarge-zarge suna da girma, don haka dole ne a gudanar da bincike mai zurfi, da adalci, kuma na gaskiya.”

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *