Daga Suleman Ibrahim Modibbo
Rahotanni a Najeriya na cewa, an sake ganin bayyana riƙaƙƙen Ɗanbindigar nan Ɓaleri wanda ya addabi yankunan Zamfara, Sokoto, da Katsina, bayan Sojojin Jamhuriyar Nijar sun ce sun kama shi.
A makon da ya gabata ne dai, jami’an tsaro a Jamhuriyar Nijar suka ce sun yi nasarar cafke ƙasurgumin ɗanbindigar Ɓaleri, wanda ake nema ruwa a jallo a Najeriya.
Dakarun runduna ta musamman da ake yi wa laƙabi da Farautar Bushiya (Faraoutar Bushiya), sun ce sun kama shi ne a garin Rigar Kowa Gwani, da ke yankin Gidan Rumji a jihar Maraɗi.
To sai dai kuma DCL Hausa mai yaɗa labarai ta Internet ta ce “Ɓaleri ya sake bayyana, a cikin wani bidiyo da DCL Hausa ta samu, an nuna Bello Turji, yana daga hannun Baleri tare da musanta ikirarin kama shi”, in ji Jaridar.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
An banka wa gidaje 24 da runbunan ajiyar hatsi wuta a jihar Jigawa bayan wani rikici ya ɓarke tsakanin Hausawa da Fulani.
-
Sojoji sun isa wasu ƙauyuka biyar a jihar Kebbi dan farwa Lakurawa, bayan sun kai harin da ya yi ajalin mutum 10.
-
Gwamantin Edo ta rushe gidan wani mutum saboda zarginsa da hannu a ayyukan garkuwa da mutane.
-
Gwamantin Kano ta ƙulla yarjejeniyar samar da sabbin motocin sufuri na zamani masu amfani da CNG.
-
Jam’iyyar PDP ta yi Alla wadai da dakatar da Sanata Natasha.