Daga Suleman Ibrahim Modibbo
Wata babbar kotun tarayya da ke zamanta a Abuja ta aika sammaci ga Gwamnan Babban Bankin Ƙasa, Olayemi Cardoso da ya bayyana a gabanta game da shari’ar da ake yi wa kamfanin crypto na Binance.
The Cable ta rawaito cewa kotun ta ce Cardoso zai bayyana gaban ta da wasu takardun bayanai a ranar 2 ga watan Satumba.
Duk da cewa, mai shari’a Emeka Nwite ya dage zaman kotun zuwa 11 ga watan Oktoba, lauyan waɗanda ake ƙara ya buƙaci kotun ta sake sanya ranar zaman.
Kotu: An Tsare Ɗan Jarida A Gidan Yari Kan Zargin Ɓata Sunan Gwamnan Kano Abba.
Gwamnatin Najeriya Ta Bai Wa Ƴan Kasuwa Wa’adin Tata Ɗaya Su Rage Farashi.
Amnesty Ta Nemi A Saki Ɗan PDPin Da Ke Tsare A Sokoto Kan Wallafa Bidiyon Gwamna Da Matarsa.
Daily Nigerian ta ce, a watan Afrilu ne dai, hukumar EFCC ta gurfanar da shugaban kamfanin Binance, Tigran Gambaryan kan zargin badaƙalar kuɗi.
Haka kuma, hukumar tattara haraji ta kasa tana tuhumar Binance da laifin kaucewa biyan haraji.
Kotun dai ta bukaci Gwamnan CBN ya bayyana gabanta ko ya tura wakilci.
Haka kuma, kotun ta mika sammaci ga shugaban sashin shari’a na CBN.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Sojoji sun isa wasu ƙauyuka biyar a jihar Kebbi dan farwa Lakurawa, bayan sun kai harin da ya yi ajalin mutum 10.
-
Gwamantin Edo ta rushe gidan wani mutum saboda zarginsa da hannu a ayyukan garkuwa da mutane.
-
Gwamantin Kano ta ƙulla yarjejeniyar samar da sabbin motocin sufuri na zamani masu amfani da CNG.
-
Jam’iyyar PDP ta yi Alla wadai da dakatar da Sanata Natasha.
-
Kswanaki biyu bayan rasa ran wasu mutum 16 a wani hatsarin mota a Abeokuta wasu ukun sun sake rasuwa in da wasu suka jikkata.