Daga Fatima Suleiman Shu’aibu
A kalla yara kanana 19 ne suka rasu sanadiyyar kamuwa da cutar Kyanda a karamar hukumar Mubi, dake Jihar Adamawa.
Kwamishinan lafiya na jihar Felix Tangwami ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Najeriya NAN a Mubi ranar Asabar cewa sama da yara 200 ne suka kamu da cutar a karamar hukumar.
Ya ce an soma samun labarin barkewar cutar ce a garin Yola, inda cikin gaggawa aka tura jami’an lafiya da magunguna domin a taro cutar kada ta yi ɓarkewar da ba za a iya shawo kansa da wuri ba.
Ya kuma ba da tabbacin cewa za a mika yaran da suka kamu da cutar zuwa snyan asibitocin jihar domin a basu kulawa.
Premium Times ta ruwaito cewa Kwamishinan ya ce tawagar likitocin za su kuma nausa zuwa karamar hukumar Gombi inda aka sake samun bullar cutar.
A karshe Tangwami ya dora laifin kin kai yara asibiti a yi wa ‘ya’ya rigakafin citar tun farko ne yi sanadiyar samun ɓarkewar cutar a yankunan jihar.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Sojoji sun isa wasu ƙauyuka biyar a jihar Kebbi dan farwa Lakurawa, bayan sun kai harin da ya yi ajalin mutum 10.
-
Gwamantin Edo ta rushe gidan wani mutum saboda zarginsa da hannu a ayyukan garkuwa da mutane.
-
Gwamantin Kano ta ƙulla yarjejeniyar samar da sabbin motocin sufuri na zamani masu amfani da CNG.
-
Jam’iyyar PDP ta yi Alla wadai da dakatar da Sanata Natasha.
-
Kswanaki biyu bayan rasa ran wasu mutum 16 a wani hatsarin mota a Abeokuta wasu ukun sun sake rasuwa in da wasu suka jikkata.