Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa (EFCC) ta kama mutane hamsin da tara da ake zargi da aikata zamba ta intanet a Abuja.
EFCC ta bayyana hakan ne a shafin ta na X a ranar Laraba.
A cewar hukumar, jami’anta daga ofishin ta na Abuja ne suka gudanar da wannan kamen a ranar Litinin 24 ga watan Fabrairu, 2025.
Hukumar ta bayyana cewa “ta kama mutanen ne a kan Titin Abacha da ke yankin Mararaba Jihar Nasarawa, bayan samun sahihan bayanai kan rawar da suke takawa a ayyukan damfara ta yanar gizo,”
A yayin wannan samamen jami’an EFCC sun kwato wayoyin salula guda saba’in da uku na nau’uka daban-daban daga hannun waɗanda ake zargin.
Hukumar ta ce za ta gurfanar da su gaban kotu da zarar bincike ya kammala.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
An banka wa gidaje 24 da runbunan ajiyar hatsi wuta a jihar Jigawa bayan wani rikici ya ɓarke tsakanin Hausawa da Fulani.
-
Sojoji sun isa wasu ƙauyuka biyar a jihar Kebbi dan farwa Lakurawa, bayan sun kai harin da ya yi ajalin mutum 10.
-
Gwamantin Edo ta rushe gidan wani mutum saboda zarginsa da hannu a ayyukan garkuwa da mutane.
-
Gwamantin Kano ta ƙulla yarjejeniyar samar da sabbin motocin sufuri na zamani masu amfani da CNG.
-
Jam’iyyar PDP ta yi Alla wadai da dakatar da Sanata Natasha.