Daga Suleman Ibrahim Moddibo
Gidauniyar Mai Tama Tugga ta karyata rade-radin da ke yawo cewa gidauniyar na da hannu wajen daukar nauyin yin zaben shugaban jam’iyyar APC a jihar Bauchi.
Hakan na zuwa ne bayan bayan wani rade-radin da ke yawo kan cewa gidauniyar na da hannu dumu-dumu wajen shirya zaben.
Saboda haka ne gidauniyar ta karyata wannan batu, Abubakar Umar, shine sakataren watsa labarai na gidauniyar a jihar Bauchi ya ce, “ Gidauniyar Ambasada Yusuf Mai Tama Tugga, bata da halaka da zaben da aka yi, imma ya wuce cewa shi Ambasada dan jam`iyyar APC ne”.
“An zabi wanda yakamata a jihar Bauchi matsayin shugaban jam`yyar APC”.
A ranar Asabar 16 ga watan Oktoba ne dai jam`iyyar APC ta zabi Sunusi Aliyu Kunde a matsayin shugabanta na jihar Bauchi.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
2023: Ni ba ɗan APC bane, martanin Jonathan ga wadanda suka saya masa form din APC.
-
Kotu tayi fatali da kara kan dakatarda Isa Kudan daga takarar Gwamna a jihar Kaduna.
-
Kotun tarayya taki bada kariya wa Gwamnan CBN kan takaran shugaban kasa.
-
Da Dumi Dumi: Kakakin Majalisar Dokokin jihar Bauchi ya fice daga APC zuwa PDP
-
Idan Na Zama Shugaban Kasar Najeriya Zan Kawo Sauyi -Tambuwal.