Daga Suleman Ibrahim Modibbo
Gidauniyar da ke tallafawa Marayu da Marasa Galihuta Orphans and Vulnerable Populations Care Foundation, a jihar Bauchi ta sallami shugaban riƙo na ƙaramar hukumar Bauchi Umar Aliyu Saraki, daga gidauniyar, bisa zargin samun sa, saɓa dokokin aiki.
Cikin wata sanarwa da Ukasha Idris Ilela, mai ɗauke da sa hannun mai magana da yawun gidauniyar Shugaban gidauniyar AmbasadaKhalifa Sani Abdullahi, ta ce korar tasa ta biyo bayan binciken da gidauniyar ta yi, inda ta same shi da saɓawa dokokin ƙungiyar.
“An same shi da aikata manyan laifuka biyar ciki da saɓa dokokin ƙungiyar kamar, da gaza miƙa bayanai game da ayyukansa, ga kamar yadda doka ta tanada”, in ji sanarwar.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
An banka wa gidaje 24 da runbunan ajiyar hatsi wuta a jihar Jigawa bayan wani rikici ya ɓarke tsakanin Hausawa da Fulani.
-
Sojoji sun isa wasu ƙauyuka biyar a jihar Kebbi dan farwa Lakurawa, bayan sun kai harin da ya yi ajalin mutum 10.
-
Gwamantin Edo ta rushe gidan wani mutum saboda zarginsa da hannu a ayyukan garkuwa da mutane.
-
Gwamantin Kano ta ƙulla yarjejeniyar samar da sabbin motocin sufuri na zamani masu amfani da CNG.
-
Jam’iyyar PDP ta yi Alla wadai da dakatar da Sanata Natasha.