Yayin da wasu al’ummar musulmi ke shirin bukukuwan Sallah bayan kammala Azumi 29 ko 30 da shagalin hawan Sallah a masarautar Bauchi da ke jihar Bauchi a Arewacin Najeriya, Gwamnatin Jihar ta sanar da soke Hawan Sallar na bana.
Albarka Radio da ke Bauchi ta rawaito cewa, sanarwar soke hawan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa ɗauke da sa hannun babban mashawarcin gwamnan jihar Bauchi a bangaren watsa labarai da Sadarwa Kwamared Mukhtar Gidado.
Sanarwar ta ce Gwamnatin Jihar Bauchi ta yi bayanin cewa daukar wannan mataki ya biyo bayan hukuncin da kwamitin kula da hawan masarautar Bauchi ya dauka ne na soke hawan ba tare da saka gwamnati a ciki ba, la’akari da tasirin hawan wajen nuna kyawawan al’adun Bauchi da ke jawo hankalin baki zuwa jihar.
Gwamnatin ta kuma ba da haƙuri ga jama’a sakamakon halin da za su samu kansu ciki sakamakon dalilin daukar wannan mataki.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Ƙudirin dokar da ke neman samar da Ofishin Firainista a matsayin Shugaban Gwamnati a Najeriya ya wuce karatu na 2 a majalisar wakilai.
-
Jami’an tsaro sun kama ɗalibai 59 a jihar Oyo
-
An dawo da ƴan Najeriya kusan 1000 gida daga ƙasar Libiya a farkon 2025 kawai
-
Masarautar Bauchi ta yi amai ta lashe kan soke hawan Sallah.
-
Kwastam ta kwace kuɗi kimanin naira biliyan 289 da aka boyi a katon ɗin yoghurt a Filin Jirgin Saman Abuja