Daga Abdul’aziz Abdullahi
Gwamnatin jihar Gombe ta kulla yarjejeniyar da wani shararren kamfani mai suna China18th Engineering, wanda zai samarwa jihar tashar wutar lantarki megawatt 100 mai amfani da hasken rana (Solar).
Gwamna Inuwa Yahaya, ya rattaba hannun kan takardar yarjejeniyar a gidan gwamnati da ke Gombe, in da ya bayyana muhimmancin samar da tashar wutar lantarkin ta fuskar bunkasa tattalin arziki da kuma magance matsalar wutar lantarki da ake yawan samu.
Gwamnan ya kuma yi tsokaci kan matsalar rashin wutar lantarki da aka samu a fadin kasar a baya-bayan nan da ya shafi Gombe da sauran sassan Arewacin Najeriya, in da ya jaddada cewa samar da tashoshin wutar lantarki mallakar jihohi za su iya dakile wannan matsala.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Ɗiyata “ta yi aiki wa Buhari shekaru huɗu a ofishin Osinbajo ba tare da ko kwabo ba-Buba Galadima
-
Arewacin Najeriya ya fi Kudanci samun muƙaman Gwamnatin Tarayya- Fadar Shugaban Ƙasa
-
NLC ta nuna damuwa kan ƙin biyan sabon albashi mafi ƙanƙanta na Naira 70,000 da wasu gwamnonin Najeriya ke yi
-
Ana zargin makiyaya sun hallaka manoma biyu a jihar Benue.
-
Sabon harin Isra’ila a Gaza ya yi ajalin mutum 35 tare da jikkata wasu 55.