Daga Suleman Ibrahim Modibbo
Gwamnan jihar Jigawa Umar Namadi, ya janye dakatarwar da ya yi wa kwamishinansa ayyuka na jihar Auwal Ɗanladi Sankara, bayan da wata kotu a jihar Kano ta wanke shi daga zargin aikata lalata.
Janye dakatarwar na kunshe ne cikin wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun sakataren gwamnatin jihar Jigawa Bala Bala Ibrahim ya ake wa manema labarai a birnin Dutse.
Sanarwar ta ce, an janye dakatarwar ne biyo bayan wanke Kwamishinan daga zargin aikata lalata da wata babbar kotun shari’ar Muslunci ta yi a Kano.
Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Jigawa Ta Raba Tallafi Ga Al’ummar Kiyawa.
Tsohon Gwamnan Jigawa Sule Lamiɗo Ya Caccaki Gwamnonin Arewacin Nijeriya Kan Zuwa Amurka.
Idan za a iya tunawa gwamna Namadi ya dakatar da Kwamishinan ne lokacin da hukumar Hisbah ta jihar Kano ta fara bincike kan wasu zarge zarge da ake masa domin bada damar yin bincike.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
An banka wa gidaje 24 da runbunan ajiyar hatsi wuta a jihar Jigawa bayan wani rikici ya ɓarke tsakanin Hausawa da Fulani.
-
Sojoji sun isa wasu ƙauyuka biyar a jihar Kebbi dan farwa Lakurawa, bayan sun kai harin da ya yi ajalin mutum 10.
-
Gwamantin Edo ta rushe gidan wani mutum saboda zarginsa da hannu a ayyukan garkuwa da mutane.
-
Gwamantin Kano ta ƙulla yarjejeniyar samar da sabbin motocin sufuri na zamani masu amfani da CNG.
-
Jam’iyyar PDP ta yi Alla wadai da dakatar da Sanata Natasha.