October 16, 2024

Warning: sprintf(): Too few arguments in /home/martabaf/public_html/wp-content/themes/elegant-magazine/lib/breadcrumbs/breadcrumbs.php on line 254

Hukumar Kula Da Shige Da Fice Ta Najeriya Ta Yi Ƙarin Girma Ga Wasu Jami’anta A Jihar Gombe.

Daga Abdul’aziz Abdullahi

A Najeriya hukumar kula da shige da fice ta ƙasar wato Nigeria Immigration Service (NIS) reshen jahar Gombe, ta yi ƙarin girma ga wasu jami’an ta domin ƙara ƙarfafa musu gwiwa akan ayyukan su.

Da ya ke jawabi a ya yin wani biki da ya gudana a dakin taro na sakatariyar gwamnatin tarayya da ke Gombe, a ranar Talata, controller janar na Hukumar Emmanuel Olayinka, ya shawarci jami’an da aka ƙarawa girman da su kasance masu biyayya ga hukumar tare da ba ta goyon baya a ayyukan da take don inganta shige da fice a ƙasar.

A dakatar da biyana fansho a matsayin tsohon gwamnan jihar Gombe, na yafe – Dankwambo ga Gwamnatin Gombe

Na Dinke Barakar da a’ke samu yayin bikin Mauludi da Wakokin Yabon Fiyayyen Halilta – Sarkin Kasidun Bauchi

Gidauniyar OVPCF Ta Tube Shugabanta Na Bauchi, Tare Da Sallamarsa Baki Ɗaya.

Mohammed Salihu Al’amin na ɗaya daga cikin jami’an hukumar wanda ya samu ƙarin matsayi daga mataimakin sufuritanda na biyu zuwa na daya ya nuna farin cikin sa, in da ya ce hakan zai ƙara zaburar da su domin tabbatar da ayyukan su tafi yadda yakamata a faɗin ƙasar nan.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *