Daga Umar Rabiu Inuwa
Nasarar Masar ta samu ta biyo bayan aikin kusan shekaru 100 da gwamnatin ƙasar da kuma al’ummatar ta su ka yi na kawo karshen cutar zazzaɓin cizon Sauro, acewar wata sanarwa da hukumar lafiya ta duniya ta fitar a jiya Lahadi.
Kasar Masar dai ita ce kasa ta uku da aka bai wa takardar shedar kubuta daga cutar zazzaɓin sauro a yankin gabashin Mediterrenean ta Hadaddiyar Daular Larabawa da Maroko, sai kuma ta farko tun shekara ta 2010.
punchng ta yawaita, a duniya baki ɗaya kasashe Arba’in da Huɗu (44) ne daga yanki daya suka kai wannan matsayin.
Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta ba da takardar shedar kawar da cutar zazzabin cizon sauron ba tare da wata shakka ba ganin cewa dama an dakile yaduwar cutar zazzabin cizon sauro wadda sauro Anopheles ke kawo wa, a duk faɗin kasar tun shekaru ukun da suka gabata.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Masarautar Bauchi ta yi amai ta lashe kan soke hawan Sallah.
-
Kwastam ta kwace kuɗi kimanin naira biliyan 289 da aka boyi a katon ɗin yoghurt a Filin Jirgin Saman Abuja
-
Fasinjojin wata mota huɗu sun riga mu gidan gaskiya wasu kuma sun jikkata a jihar Borno.
-
Yan Sandan Jihar Kaduna sun kama Ƴan Daba bisa zargin kai wa masu ibadar Sallar Tahajjud hari.
-
Kotun Ƙoli ta raba gardama kan rikicin Sakataren jam’iyyar PDP na tarayyar Najeriya.