Daga Zainab Adam Alaramma
Hukumar tace fina-fina da daf’i ta jihar Kano ta wanke Jarumar masana’antar Kannywood Maryam Yahaya bisa wani zargi da akai mata na rungumar wani saurayi a cikin wani bidiyo.
Abdullahi Sani Sulaiman, wanda shine Mai magana da yawun hukumar ne ya bayyana hakan ga freedom Radio
Ya ce, an kai musu korafi akan jaruma Maryam Yahaya kan wani bidiyo da ake yadawa a kafafen Sada Zumunta, Inda aka ga wani yana rungumar wata wacce ake zargin Maryam Yahaya ce, amma sun gudanar da bincike sun gano cewa ba Maryam Yahaya ba ce a cikin bidiyon.
Abdullahi Sani Sulaiman ya ƙara da cewa, shugaban hukumar tace fina-fina ta jihar kano Abba El-Mustapha ya baiwa daraktan dake kula da Yan masana’antar Kannywood damar gudanar da bincike don tabbatar da anyi adalci ga kowanne bangare.
Binciken dai ya wanke Maryam Yahaya saƙal, inda ya ce, bayan kammala binciken hukumar sun ta tabbatar da cewa Wacce ake zargin ba jaruma Maryam Yahaya ba ce, don haka suka ga dacewar su fito su shaidawa duniya cewa ba Maryam bace, saboda abun ya yadu da yawa bai dace su yi shuru akan maganar ba.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
An banka wa gidaje 24 da runbunan ajiyar hatsi wuta a jihar Jigawa bayan wani rikici ya ɓarke tsakanin Hausawa da Fulani.
-
Sojoji sun isa wasu ƙauyuka biyar a jihar Kebbi dan farwa Lakurawa, bayan sun kai harin da ya yi ajalin mutum 10.
-
Gwamantin Edo ta rushe gidan wani mutum saboda zarginsa da hannu a ayyukan garkuwa da mutane.
-
Gwamantin Kano ta ƙulla yarjejeniyar samar da sabbin motocin sufuri na zamani masu amfani da CNG.
-
Jam’iyyar PDP ta yi Alla wadai da dakatar da Sanata Natasha.