Hukumar karɓar Ƙorafe-ƙorafe da Yaƙi da Cin Hanci ta Jihar Kano ta kama Shugaban Karamar Hukumar mulkin Kiru Alhaji Abdullahi Mohammed, a ranar Jumma’a bisa zargin sayar da fili na fiye da naira miliyan darai, da aka tanada domin yin filin wasa na Kafin Maiyaki.
Jaridar internet ta Solacebase ta rawaito mai magana da yawun hukumar Malam Kabir Abba Kabir, ya shaida wa mata cewa, an tsare shugaban ƙaramar hukumar kuma ana masa tambayoyi.
Ya bayyana cewa binciken hukumar ya gano cewa an saka kuɗaɗen ne kai tsaye zuwa asusun bankin Mohammed.
Kabir ya kuma bayyana cewa wani kamfani mai suna Mahasum da wasu mutane ne suka sayi filayen da aka ware domin filin wasar.
Ya bayyana cewa asusun bankin Mohammed ya karɓi fiye da naira miliyan 240 daga ranar 1 ga watan Nuwamba, 2024, lokacin da aka rantsar da shi, zuwa 27 ga watan Fabrairu, kuma an riga an kwato su.
Kabir ya ƙara da cewa Mohammed ya na ba da haɗin kai wajen binciken da hukumar ke yi, wanda ke da nufin gano gaskiyar cinikin filayen, da kuma gurfanar da masu hannu a wannan badaƙala a gaban shari’a.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Ƙudirin dokar da ke neman samar da Ofishin Firainista a matsayin Shugaban Gwamnati a Najeriya ya wuce karatu na 2 a majalisar wakilai.
-
Jami’an tsaro sun kama ɗalibai 59 a jihar Oyo
-
An dawo da ƴan Najeriya kusan 1000 gida daga ƙasar Libiya a farkon 2025 kawai
-
Masarautar Bauchi ta yi amai ta lashe kan soke hawan Sallah.
-
Kwastam ta kwace kuɗi kimanin naira biliyan 289 da aka boyi a katon ɗin yoghurt a Filin Jirgin Saman Abuja