Daga Suleman Ibrahim Modibbo.
Yayin da ƙasar Maroko ke bikin samun ƴancin kai, ma’aikatar shari’a ta kasar ta sanar da yi manoma tabar Wiwi kusan dubu 5 afuwa.
An samu manoman da laifin noma tabar Wiwi ba tare da wani izini ba daga hukumomi abin da kai ga tuhumar su.
An yi wa Manoman afuwa su sama da duba huɗu da 800 ne a jajibirin bikin ranar da Moroko ta samun ƴancin kai, in da Mai Alfarma Sarki Muhammad, na 6 ya dauki wannan mataki saboda dalilai na jinkai.
Wasu daga cikin Manoman dubu 4 da 831, tuni aka yanke musu hukuncin dauri a gidan yari bayan an tabbatar da laifukansu, yayin da ake gudanar da bincike a kan wasu, bisa dalilan cewa sun mallakin manyan filaye da ake gudanar da noman tabar wuiwui a cikinsu.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
An banka wa gidaje 24 da runbunan ajiyar hatsi wuta a jihar Jigawa bayan wani rikici ya ɓarke tsakanin Hausawa da Fulani.
-
Sojoji sun isa wasu ƙauyuka biyar a jihar Kebbi dan farwa Lakurawa, bayan sun kai harin da ya yi ajalin mutum 10.
-
Gwamantin Edo ta rushe gidan wani mutum saboda zarginsa da hannu a ayyukan garkuwa da mutane.
-
Gwamantin Kano ta ƙulla yarjejeniyar samar da sabbin motocin sufuri na zamani masu amfani da CNG.
-
Jam’iyyar PDP ta yi Alla wadai da dakatar da Sanata Natasha.