Hamas ta miƙa gawarwakin Isra’ilawa huɗu da aka tsare a Gaza ga Kungiyar Agaji ta Red Cross, a matsayin wani bangare na ƙarshe a matakin farko na yarjejeniyar tsagaita wuta.
A lokaci guda, bas ɗin farko dauke da Palasdinawa fursunoni da aka sako daga gidan yari na Ofer ya isa birnin Ramallah, da ke yankin Gabar Yamma da Isra’ila ke mamaye da shi.
Wannan musayar na zuwa ne bayan Hamas ta sanar da cimma yarjejeniya da makwatan su kan sakin fursunoni 620 na Falasdinu da ya kamata a sako daga Isra’ila a makon da ya gabata, da kuma yawan dai dai da hakan na mata da yara da aka tsare tun lokacin da yaƙi ya barke. Isra’ila ta tabbatar da yarjejeniyar ba tare da bayar da ƙarin bayani ba.
Kakakin Majalisar Dinkin Duniya Stephane Dujarric, ya buƙaci Isra’ila da ta bar ƙarin tantuna da mafaka su shiga Gaza bayan da jarirai shida ƴan Falasdinu suka mutu sakamakon tsananin sanyi.
Ma’aikatar Lafiya ta Gaza ta tabbatar da cewa Falasinawa dubu arba’in da takwas da dari uku da arba’in da takwas sun mutu a yakin da Isra’ila ke kaiwa Gaza, yayin da wasu dari daya da goma sha daya da dari bakwai da sittin da daya suka jikkata.
Ofishin Watsa Labarai na Gwamnatin Gaza ya sabunta alkaluman adadin mace-macen zuwa akalla 61,709, ya na mai cewa dubban mutane da ke ƙarƙashin baraguzan gine-gine ana kyautata zaton sun mutu.
A bangaren Isra’ila mutane 1,139 ne aka kashe a hare-haren Hamas na ranar 7 ga watan Oktoba 2023, kuma fiye da 200 aka kama a matsayin fursunoni.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
An banka wa gidaje 24 da runbunan ajiyar hatsi wuta a jihar Jigawa bayan wani rikici ya ɓarke tsakanin Hausawa da Fulani.
-
Sojoji sun isa wasu ƙauyuka biyar a jihar Kebbi dan farwa Lakurawa, bayan sun kai harin da ya yi ajalin mutum 10.
-
Gwamantin Edo ta rushe gidan wani mutum saboda zarginsa da hannu a ayyukan garkuwa da mutane.
-
Gwamantin Kano ta ƙulla yarjejeniyar samar da sabbin motocin sufuri na zamani masu amfani da CNG.
-
Jam’iyyar PDP ta yi Alla wadai da dakatar da Sanata Natasha.