March 13, 2025

Warning: sprintf(): Too few arguments in /home/martabaf/public_html/wp-content/themes/elegant-magazine/lib/breadcrumbs/breadcrumbs.php on line 254

Jami’an tsaro sun ceto manoma 36 daga hannun ƴan bindiga a Kebbi.

Daga Fatima Suleiman Shu’aibu

Tawagar haɗin gwiwa ta ’yan sanda, sojoji da ’yan sa-kai, sun ceto manoma 36 da ’yan bindiga su ka sace a ƙaramar Hukumar Danko/Wasagu a Jihar Kebbi.

Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, SP Nafiu Abubakar, ya bayyana cewa ’yan bindiga sun tare manoman da ke dawowa daga gonakinsu, inda suka yi awon gaba da su.

Rundunar haɗin gwiwar ta yi gaggawar kai ɗauki, inda suka yi nasarar fatattakar ’yan bindigar zuwa cikin daji, yayin da wasu daga cikinsu suka tsere da raunukan harbin bindiga.

Babban hafsan Sojin ƙasa ya sha alwashin kawo ƙarshen Ƴan ta’addan Lakurawa cikin kankanin lokaci.

Sojojin Najeriya sun yi raga-raga da sansanonin ƴan bindiga a jihar Taraba.

Sojan saman Nijeriya sun yi wa Ƴan Boko Haram fata-fata a Borno.

Sanarwar ta tabbatar da cewa an ceto dukkanin manoma 36 ba tare da sun samu rauni ba, kuma an miƙa su ga iyalansu.

Kwamishinan ’yan sandan jihar, Bello M. Sani, ya yi kira ga dukkanin hukumomin tsaro a yankin da su ƙara haɗa kai don yaƙi da ’yan bindiga da sauran masu aikata miyagun laifuka.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *