Kwamitin Gudanarwa na Kasa na jam’iyyar A. A ya yaba da hukuncin da Kotun sauraren kararrakin Zaben Gwamnan jihar Edo ta yanke, na ƙin amincewa da karar da wasu mambobin jam’iyyar karkashin jagorancin Adekunle Rufai Omoaje suka shigar, suna ƙalubalantar nasarar Gwamnan jihar Edo Monday Okpebholo.
Jaridar Leadership ta ruwaito cewa shugaban jam’iyyar na ƙasa Chief Kenneth Udeze, ya jaddada cewa jam’iyyar A. A ko ɗan takarar ta na gwamna a jihar Edo ba su taba shigar da wata ƙara ba, da ke ƙalubalantar nasarar Okpebholo.
Jam’iyyar Action Alliance ta kara da cewa ƙarar da aka yi watsi da ita yunkuri ne na wasu mutanen da ba a san su ba, ƙarkashin jagorancin wani mai suna Adekunle Omoaje wanda ba ɗan takarar jam’iyyar ba ne, don bata sunan jam’iyyar.
Ya ce: “A ko da yaushe, Action Alliance ko dan takarar ta na gwamna a jihar Edo ba su taba shigar da wata ƙara ba da ke ƙalubalantar sakamakon zaben.”
Ya ce “Jam’iyyar ta yi mamakin rahoton da ke yawo a kafafen yaɗa labarai. A bayyana wa kowa cewa Adekunle Omoaje ya shigar da karar ne bisa raɓin kansa, yana ganin saka sunan jam’iyyar Action Alliance zai ba shi karfi.”
Udeze ya taya Okpebholo murna bisa nasarar da ya samu, tare da neman al’umma da su yi watsi da ƙarar da Adekunle Omoaje ya shigar, wanda ya ce jam’iyyar ba ta san shi ba.
Jam’iyyar ta kuma bayyana cewa ɓangaren shari’a shi ne zuciyar adalci a cikin al’umma, kuma bazata yarda da shari’ar banza da sunan siyasa ba.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Gwamnatin Kano ta tabbatar da za ta yi adalci da sauraron ƙorafe-ƙorafen al’ummar da aikin magance zai zayar ƙasa zai shafa a Bulbula tare da biyan diyya
-
Buba Galadima ya ƙaryata batun komawar Kwankwaso APC da Ganduje ya yi
-
NSCDC ta tura Jami’ai 415 a Zamfara don tabbatar da tsaro lokacin bukukuwan Easter
-
Ƴansandan Najeriya Najeriya sun cafke mutum biyu kan rikicin baya-bayan nan da ya afku a jihar Filato
-
Shugaba Tinubu ya ƙaddamar da sabon kwamitin ƙidaya