Hukumar zaben mai zaman kanta ta kasa INEC ta ayyana kakakin majalisar dokokin jihar Bauchi Rt. Hon. Abubakar Y Sulaiman a matsayin wanda ya lashe zaben Mazabar Ningi ta tsakiya a zaben daya gudana ranar Asabar.
Da yake sanar da sakamakon zaben, Baturen zaben Prof. Shuaibu Muhammad yace Kakakin Majalisar na Jamiyyar PDP ya samu kuri’a 16,866 daya doke abokan karawar sa na APC Hon. Khalid Abdulmalik Ningi daya samu kuri’a 15,065 da Hon. Danlami Garba Bara’u na NNPP daya samu kuri’u 4,886.
Cikin jawabinsa na godiya bayan sanar da sakamakon Abubakar Sulaiman ya yi godiya wa Allah daya bashi wannan nasarar da jinjinawa al’ummar mazabar sa bisa zabar sa da suka sake yi.
Abubakar Y Sulaiman ya yi kira wa sauran abokan takarar sa dasu zo su hada hannu don ciyar da karamar hukumar Ningi gaba.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Tinubu ya rantsar da sabon Sakataren Gwamnatinsa Akume
-
Kungiyar Ƴan Jarida ta ƙasa NUJ za ta bi sa sahun Kungiyar Kwadago NLC don Tsunduma yajin aiki kan cire tallafin Mai
-
Tsohuwar Ministar mata Pauline Tallen ta shiga hannun EFCC kan zargin Almundahana
-
Kotu Ta Bawa Ƴan Sanda Umarnin Kama Sheikh Idris Dutsen Tanshi Bisa Rainata.
-
Bayan Shan Rantsuwa Tinibu Ya Ce Daga Yanzu Gwamnatinsa Za Ta Soke Tallafin Man Fetur.