Daga Suleman Ibrahim Modibbo
Hukumar Ta Ce Fina-finai ta jihar Kano da ke Arewacin Najeriya, ta koka kan sumame da hukumar Hisbah ke kaiwa gidajen Gala a jihar, a wani mataki na kawo karshen ayyukan baɗala.
Tin da farko hukumar Hisbah ta kai sumame wasu gidajen rawa inda ta kama Ƴan Gala 15 a unguwar Fanshekara da ke birnin Kano.
Freedom Radio ta rawaito cikin wata sanarwa da Kakakin Hukumar ta ce fina-finan Malam Abdullahi Sani Sulaiman, ta fitar Lahadin ƙarshen mako ta ce “ƙorafe-ƙorafen da Hukumar ke samu daga masu gidajen Gala ya yi yawa kan yadda Hisbah ke kai sumame su kame masu Gala da kayan aikinsu.”
Sanarwar ta kuma ƙara da cewa, doka ce ta kafa Gidajen Gala a ƙarƙashin kulawar Hukumar Tace Finafinai kuma ta ba su damar gudanar da ayyukansu ba tare da cin zarafi ko tsangwama ba.
Kuma doka ta sanya wa masu Gidajen Galar Sharuɗa waɗanda in sun karya hukuncin zai hau kansu, hakan na cikin manyan dalilan da ya sa aka kafa Hukumar Tace Finafinai.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
An banka wa gidaje 24 da runbunan ajiyar hatsi wuta a jihar Jigawa bayan wani rikici ya ɓarke tsakanin Hausawa da Fulani.
-
Sojoji sun isa wasu ƙauyuka biyar a jihar Kebbi dan farwa Lakurawa, bayan sun kai harin da ya yi ajalin mutum 10.
-
Gwamantin Edo ta rushe gidan wani mutum saboda zarginsa da hannu a ayyukan garkuwa da mutane.
-
Gwamantin Kano ta ƙulla yarjejeniyar samar da sabbin motocin sufuri na zamani masu amfani da CNG.
-
Jam’iyyar PDP ta yi Alla wadai da dakatar da Sanata Natasha.