Daga Suleman Ibrahim Modibbo
Tsohon Gwamnan jihar Kogi, Yahaya Bello ya musanta zarge-zargen da hukumar EFCC ke yi masa guda 16 bayan an gurfanar da shi gaban kotu a Abuja a yau Laraba.
EFCC ta gurfanar da Bello bisa zargin laifuka 16 da suka hada da karkatar da kudade da su ka kai Naira biliyan 110.
Sauran wadanda ake tuhuma tare da Bello sun hada da Umar Shoaib Oricha da Abdulsalami Hudu, wadanda su ma su ka musanta -tuhumen.
EFCC ta gurfanar da tsohon Gwamnan Kogi Yahaya Bello a Kotu kan almundahana da naira biliyan 110.
An tsagaita bude wuta a Lebanon bayan cimma yarjejeniya tsakanin Isra’ila da Hesbollah.
Ƴarsanda ta yi barazanar kashe kanta da ƴaƴanta.
Joseph Daudu, lauyan Bello, ya miƙa rokon neman ba da belin wanda ya ke karewa, amma sai lauyan EFCC Kemi Pinheiro ya soki rokon.
Daga ƙarshe Kotun ta ba da umarnin ci gaba da tsare Yahaya Bello har sai 10 ga watan Disamba, in da za koma domin ci gaba da sauraron ƙarar.
A ranar Alhamis ne hukumar ta tabbatar da kama Yahaya Bello wanda ta ce ta tsare shi, an jima ana wasan ɓuya tsakanin sa da hukumar wadda take neman sa ruwa a jallo tun a watan Afrilun 2024.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
EFCC ta gurfanar da wasu mutum biyu kan zargin damfara da sunan A’A Rano
-
APC ta rufe hedkwatarta da ke Abuja.
-
An hallaka mutum 1 wani kuma ya jikkata kan zargin satar kare a jihar Bauchi.
-
Ɗiyata “ta yi aiki wa Buhari shekaru huɗu a ofishin Osinbajo ba tare da ko kwabo ba-Buba Galadima
-
Arewacin Najeriya ya fi Kudanci samun muƙaman Gwamnatin Tarayya- Fadar Shugaban Ƙasa