Babbar kotun Tarayya da ke zaman ta a Gyaɗi-gyaɗi a Kano ta umarci Gwamnatin jihar ta biya ƴan Kassuwar da ke da shaguna a filin Masallacin Idi da ke Ƙofar Mata Naira Biliyan 30 bisa rushe musu shaguna ba bisa ƙa’id ba.
Freedom Radio ta rawaito, a yayin zartar da hukuncin Mai Shari’a Simon Ameboda ya ce bin dare tare da rushe shagunan talakawa haramtaccen aiki ne mai cike da tsantsar zalunci da ƙeta, don haka lallai Gwamnati ta biya masu shagunan.
Haka kuma kotun ta hana Gwamnatin Kano shiga cikin filayen da yin tasirifi da shagunan balle bayar da su ga wani.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Dokin rundunar Sojin Najeriya mai muƙamin Sajan ya mutu a Kaduna.
-
Ɓarawo ya mutu yayin da ya ke ƙoƙarin sata a cikin Taransifoma.
-
Yansadan jihar Adamawa sun fara bincike kan wasu mutum 2 da zargin sun yi wa yara mata biyu Fyade.
-
Yayin da Ƴansandan Kano su ka gargaɗi al’umma kan shiga cunkoso saboda barazanar tsaro gwamnatin jihar ta ce taron Mauludin Shehu Inyass ya na nan daram.
-
Wata gobarar tankar fetur ta ƙone direbanta a Ibadan.