Daga Suleman Ibrahim Modibbo
Wata babbar kotun jihar Bauchi mai lamba biyar a karkashin jagorancin mai shari`a Mu`azu Abubakar, ta yanke wa wani matashi mai suna Umar Hardo, mazaunin unguwar Sarakuna a birnin Bauchi, hukuncin zaman gidan gyaran hali na dindindin, sakamakon samunsa da laifin yin fashi da makami.
Ti nda farko dai gwamnatin jihar Bauchi ce ta yi karar matashin gaban kotun ta hannun ma`aikatar shari`a ta jihar Bauchi, bisa tuhume-tuhume guda biyu.
Yin fashin babur a hanyar zuwa Dass ga wani mai suna Idris Abdullahi, mazaunin hanyar Gombe, ta hanayar amfani da bindiga kirar hannu da kuma rike makami da harsashai guda uku kirar gida, a ranar biyar ga watan shidan shekarar 2021, wanda aikata hakan laifi ne da ya saba da kashi daya biyu cikin baka da kashi biyu na hukuncin rike makami ba tare da izini ba, da kuma sabawa sashi na kashi uku daya cikin baka.
Alkalin kotun mai shari`a Mu`azu Abubakar ya yanke masa hukuncinne bayan saurarar shedun masu kara.
Sai dai kuma har zuwa lokacin hada wannan labarin matashin bai daukaka kara ba kamar yadda doka ta bashi dama,
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Kotu Ta Daure Wani Matashi Watanni 15 Kan Shiga Gidan Tsohon Gwamnan Jihar Bauchi M.A.
-
Amaryar Ta Rasa Idonta Daya Ne Ana Tsaka Da Bikinta Sai Dai Duk Da Haka An Daura Mata Aure Da Angonta.
-
Zargin Taimakawa Ta’addanci: SSS Sun Mamaye Hedikwatar Babban Bankin Najeriya.
-
Gwamna Bala ya sha alwashin inganta tsaro, yaƙi da talauci, yayi yaƙin neman zaɓe a Itas
-
Ciyar Da Jihar Bauchi Gaba Ne Muradin Mu, Ku Sake Ba Mu Dama – Saƙon Gwamna Bala Ga Al’umar Udubo