Kotun sauraron laifuffukan fyade da cin zarafi da ke Ikeja a Jihar Legas, ta yanke wa wani mutum mai suna Ifeanyi Ndieze hukuncin daurin rai da rai saboda samun shi da laifin yi wa yarinya mai shekara hudu fyaɗe.
Alkalin kotun, Mai Shari’a Abiola Soladoye, ta ce mutumin ya yi wa yarinyar fyade ne a cikin coci.
Alkalin ta ce kotun ta tabbatar da tuhumar da ake yi wa wacce ta saba da sashe na 261 na kundin manyan laifuffuka na jihar Legas na 2015.
Mai Shari’a Abiola ta ce yarinyar da aka yi wa fyaden ce ta gane mutumin da cewa ya ci mata zarafi ta hanyar cusa mata ɗan yatsa a gabanta yayin ibada a cocin.
“Daga baya an kai ta gida, amma lokacin da mahaifiyarta ta yi mata wanka, sai ta ga tana zubar da jini babu kakkautawa. A asibitin ne likitoci suka ba da shawarar a kai batun gaban ’yan sanda.
“Wannan mutumin tataccen makaeyaci ne, kuma kotu ta sane shi da aikata laifin, don haka ta yanke masa hukuncin daurin rai da rai,” in ji alkalin.
Tun da farko, lauyar gwamnati, Olufunke Adegoke, ta shaida wa kotun cewa an aikata laifin ne a cocin da ke kan titin Salau Street, ranar 29 ga watan Oktoban 2020.
Jaridar Aminiya
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
An banka wa gidaje 24 da runbunan ajiyar hatsi wuta a jihar Jigawa bayan wani rikici ya ɓarke tsakanin Hausawa da Fulani.
-
Sojoji sun isa wasu ƙauyuka biyar a jihar Kebbi dan farwa Lakurawa, bayan sun kai harin da ya yi ajalin mutum 10.
-
Gwamantin Edo ta rushe gidan wani mutum saboda zarginsa da hannu a ayyukan garkuwa da mutane.
-
Gwamantin Kano ta ƙulla yarjejeniyar samar da sabbin motocin sufuri na zamani masu amfani da CNG.
-
Jam’iyyar PDP ta yi Alla wadai da dakatar da Sanata Natasha.