Daga Fatima Suleiman Shu’aibu
Ƙungiyar Malaman Kwalejin Fasaha reshen Jihar Kano, ta shiga yajin aikin gargaɗi na mako biyu da zai fara daga ranar 2 ga Disamba, 2024.
Wannan mataki an bayyana shi ne a cikin wata sanarwa da sakataren yaɗa labarai na ƙungiyar, Babangida Sa’adu, da ya sanya hannu, kuma aka rabawa manema labarai a Kano.
An yanke shawarar shiga wannan yajin aikin ne a taron NEC na 112 na ASUP da aka gudanar a Abuja ranar 28 ga Nuwamba, 2024
Gwamnatin Kano ta dawowa da Jami’ar Yusuf Maitama University sunanta na asali Northwest University.
Kungiyar ASUU reshen jihar Bauchi ta shiga yajin aikin sai baba ta gani.
ASUU ta nuna damuwa kan yawaitar ɗaliban da ke samun sakamakon first-class a Najeriya.
A lokacin wannan yajin aiki, dukkanin harkokin karatu a Polytechnic ta jihar Kano za su tsaya cik.
ASUP ta ta ba bai wa gwamnatin tarayya da sauran hukumomin da abin ya shafa wa’adin kwana 15 don sake duba da janye manufofin da su ka saɓa wa dokar Polytechnics da sauran dokokin gudanarwa a wannan bangaren.
Kungiyar ta zargi Gwamnati da rashin ɗa’a da kuma raina wasu muhimman dokokin da su ka kafa manyan makarantu mallakin jihohi da sauran kayan aikin gudanarwa.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Peter Obi ya gode wa Ƴansanda kan janye gayyatar da su ka yi wa Sarki Sunusi.
-
SERAP ta buƙaci Tinubu da ya ƙi amincewa da bashin dala biliyan $1.08 da Bankin Duniya ya amince da shi kwanan nan.
-
Wani mayaudari ya damfari Bobrisky Dalar Amurka 990.
-
Rasuwar Sheikh Idris: mun “fawwala komai ga Allah maɗaukakin Sarki”- Gwamnan jihar Bauchi.
-
Kotun koli ta soke hukuncin da ya bai wa tsagin da ke adawa da Obi a jam’iyyar LP nasara