Daga Suleman Ibrahim Modibbo
Wasu ƴanbindiga sun sace akalla mutum 30 da suka haɗa da maza da mata tare da dabbobi masu yawa a jihar Katsina.
BBC ta rawaito, lamari ya faru ne a garin Unguwar Daudu da ke cikin karamar hukumar Funtuwa da tsakar daren ranar Alhamis.
Mutane a yankin na cikin zulumi ganin cewa ba su iya zuwa gonaki ɗauko abubuwan da suka noma sanadiyar hare-hare da yin gurkuwa da jama’a da ‘yan bindigar ke yi domin neman kuɗin fansa.
Ƴan bindiga Sun Sanya Harajin Miliyan 10 Ga Wasu Ƙauyuka A Jihar Katsina.
Ƴansanda Sun Kama Wani Ɗan Kasar Aljeriya Da Bindigu A Zamfara.
Bayan abun da ya faru a garin na Unguwar Daudu, a garin Mai ruwa da ke maƙwabtaka da ƙauyen ƴan bindigar sun yi awon gaba da wasu mutane da su ka je daukar albarkatun gona a daji.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Tsohon mai horar da ƙungiyar ƙwallon ƙafar Najeriya Christian Chukwu ya rasu
-
EFCC ta gurfanar da wasu mutum biyu kan zargin damfara da sunan A’A Rano
-
APC ta rufe hedkwatarta da ke Abuja.
-
An hallaka mutum 1 wani kuma ya jikkata kan zargin satar kare a jihar Bauchi.
-
Ɗiyata “ta yi aiki wa Buhari shekaru huɗu a ofishin Osinbajo ba tare da ko kwabo ba-Buba Galadima