Daga Suleman Ibrahim Modibbo
Wasu ƴanbindiga sun sace akalla mutum 30 da suka haɗa da maza da mata tare da dabbobi masu yawa a jihar Katsina.
BBC ta rawaito, lamari ya faru ne a garin Unguwar Daudu da ke cikin karamar hukumar Funtuwa da tsakar daren ranar Alhamis.
Mutane a yankin na cikin zulumi ganin cewa ba su iya zuwa gonaki ɗauko abubuwan da suka noma sanadiyar hare-hare da yin gurkuwa da jama’a da ‘yan bindigar ke yi domin neman kuɗin fansa.
Ƴan bindiga Sun Sanya Harajin Miliyan 10 Ga Wasu Ƙauyuka A Jihar Katsina.
Ƴansanda Sun Kama Wani Ɗan Kasar Aljeriya Da Bindigu A Zamfara.
Bayan abun da ya faru a garin na Unguwar Daudu, a garin Mai ruwa da ke maƙwabtaka da ƙauyen ƴan bindigar sun yi awon gaba da wasu mutane da su ka je daukar albarkatun gona a daji.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
An banka wa gidaje 24 da runbunan ajiyar hatsi wuta a jihar Jigawa bayan wani rikici ya ɓarke tsakanin Hausawa da Fulani.
-
Sojoji sun isa wasu ƙauyuka biyar a jihar Kebbi dan farwa Lakurawa, bayan sun kai harin da ya yi ajalin mutum 10.
-
Gwamantin Edo ta rushe gidan wani mutum saboda zarginsa da hannu a ayyukan garkuwa da mutane.
-
Gwamantin Kano ta ƙulla yarjejeniyar samar da sabbin motocin sufuri na zamani masu amfani da CNG.
-
Jam’iyyar PDP ta yi Alla wadai da dakatar da Sanata Natasha.