Daga Suleman Ibrahim Modibbo
A jihar Kano da ke Najeriya, jam’iyyar NNPP, ta yi kira ga dukkanin masu sha’awar tsayawa takarar shugabancin ƙaramar hukuma ko kansila, ƙarƙashin tutar jam’iyyar da su yi gaggawar ajiye mukaman da suke riƙe da su na gwamnati nan take ko kuma kafin ƙarshen watan nan na Agustan 2024.
Kafafen yaɗa labarai a jihar Kano, sun rawaito cewa, shugaban jam’iyyar NNPP na Jihar Kano Dr. Hashim Suleiman Dungurawa, ne ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai daya gudana a birnin Kano domin bayyana matsayar jam’iyyar dangane da dokar hukumar zabe mai zaman kanta ta Kano KANSIEC.
Za a yi zaɓen ƙananan hukumomin jihar ne a watan Nuwamba, in da hukumar zaben jihar ta ce za ta yi gwajin shan kwaya ga masu sha’awar tsaya wa takarar shugabancin ƙaramar hukuma ko kansila.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
PDP ta sake dage taron Kwamitin Zartaswar ta na Kasa (NEC) zuwa ranar 15 ga watan Mayu.
-
Mijin Sanata Matasha ya buƙaci Akpabio da ya girmama matar sa.
-
Tinubu ya ya tabbatar da cewa tattalin arziƙin Najeriya ya na farfaɗo wa.
-
Ba zan yi musayar yawu da El-Rufai ba,-Ribadu
-
“Dubban mutane na shigowa jam’iyyar mu, ba da daɗewa ba, za mu karɓi manyan jiga-jigan NNPP da kansu”-Ganduje