Daga Fatima Suleiman Shu’aibu
Tsohon Shugaban Najeriya, Olusegun Obasanjo, ya yi kira da a yi garambawul na gaba ɗaya ga tsarin zaɓen ƙasar.
Da yake jawabi a taron Chinua Achebe Leadership Forum, Jami’ar Yale, a Amurka, Obasanjo ya yi kira musamman da a tsige Mahmood Yakubu, Shugaban Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC), da sauran jami’ai a duk matakai.
A lokacin da yake bayyana zaɓen 2023 a matsayin “abun kunya,” Obasanjo ya jaddada muhimmancin sake fasalin tsarin zaɓen domin dawo da sahihanci da amincewa.
Kwankwaso Ya Yi Zargin Ana Neman Yi Musu Dole Daga Lagos A Harkar Masarautun Kano.
Tsadar Rayuwa: Ba Da Daɗewa Ba Abubuwa Za Su Yi Kyau -Gwamnatin Najeriya.
Ƙungiyar Ma’aikatan Jami’o’in Da Kwalejojin Najeriya Sun Janye Yajin Aiki
Haka nan, tsohon shugaban ya ba da shawarar a rage tsawon wa’adin shugabannin INEC da kuma aiwatar da cikakken bincike kafin a naɗa mutane, domin hana naɗin waɗanda ke da ra’ayin ɓangaranci.