Gwamnan jihar Bauchi Sen. Bala Abdulkadir Mohammed, ya miƙa sakon ta’aziyarsa bisa rasuwar Dr. Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi Bauchi.
Gwamna Bala cikin sakon daya wallafa a shafinsa na Facebook ya nuna alhini bisa rasuwar malamin.
Yace “Cikin alhini tare da fawwala komai ga Allah maɗaukakin Sarki, mun wayi gari da rasuwar ɗaya daga cikin malaman addinin Musulunci daga nan jihar Bauchi, Sheik Idris Abdulaziz Dutsen Tanshi, bayan fama da jinya.”
“Yayin da muke roƙa masa gafarar Allah maɗaukakin Sarki, a madadin ni kaina, iyali gwamnati da ɗaukacin al’ummar Bauchi, ina isar da ta’aziyya ga iyalan marigayi Malam da almajiran sa. Allah ya ba mu haƙurin juriya, ya haskaka kabarin sa.” Cewar Gwamnan Bala.
Gwamnan yayi addu’ar Idan ajali ya riske mu, ya Allah ka sa mu cika da imani, Amin.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Gwamnatin Kano ta tabbatar da za ta yi adalci da sauraron ƙorafe-ƙorafen al’ummar da aikin magance zai zayar ƙasa zai shafa a Bulbula tare da biyan diyya
-
Buba Galadima ya ƙaryata batun komawar Kwankwaso APC da Ganduje ya yi
-
NSCDC ta tura Jami’ai 415 a Zamfara don tabbatar da tsaro lokacin bukukuwan Easter
-
Ƴansandan Najeriya Najeriya sun cafke mutum biyu kan rikicin baya-bayan nan da ya afku a jihar Filato
-
Shugaba Tinubu ya ƙaddamar da sabon kwamitin ƙidaya