Nijeriya ta bukaci masu hannu da shuni a fadin duniya da su tallafawa kasashen Afrika da sauyin yanayi ya shafa.
Mataimakin shugaban majalisar wakilai ta kasa, Benjamin Okezie Kalu kuma shugaban tawagar Nijeriya a ci gaba da zaman majalisar wakilai daga kasashen Afrika dake gudana a kasar Afrika ta Kudu a ranar Talata inda ya bayyana matsayar kasar.
Da yake jawabi kan makalar da aka gabatar mai taken “Tasirin sauyin yanayi da tsarin Afrika na zuwa COP”, wanda daraktan shirye shirye da bincike na PACJA, Mista Charles Mwangi Nyambura ya gabatar, Kalu ya bada shawarar karbar haraji kan sauyin yanayi a kasashe masu rauni na Afrika.
Mataimakin shugaban majalisar, wanda ya koka kan ambaliyar ruwa da ta faru a jihar Borno da Zamfara ya ce shawarar harajin na sauyin yanayi zai taimaka wajen rage radadin da sauyin yanayi ya haifar a yankin.
Ya ce: ” Afrika ta tasirantu da illa na sauyin yanayi duk da cewa tana bada kashi 3.8 ga batun fitar da iskar idan aka kwatanta da kasar China dake fitar da kaso 23 da kasar Amurka mai fitar da kaso 19 da Turai mai kaso 13.
“Sauyin yanayi ya hana Afrika samun ci gaba da fimma muradin karni gami da walwalar mutane.
” A yau, kusan ‘yan Afrika Miliyan 600 basa samun wutar lantarki kamar yadda Bankin duniya ya fada”.
Jagoran na tawagar Nijeriya ya kuma bayyana illar da karancin abinci ke yi wanda sauyin yanayi ya haifar.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
An banka wa gidaje 24 da runbunan ajiyar hatsi wuta a jihar Jigawa bayan wani rikici ya ɓarke tsakanin Hausawa da Fulani.
-
Sojoji sun isa wasu ƙauyuka biyar a jihar Kebbi dan farwa Lakurawa, bayan sun kai harin da ya yi ajalin mutum 10.
-
Gwamantin Edo ta rushe gidan wani mutum saboda zarginsa da hannu a ayyukan garkuwa da mutane.
-
Gwamantin Kano ta ƙulla yarjejeniyar samar da sabbin motocin sufuri na zamani masu amfani da CNG.
-
Jam’iyyar PDP ta yi Alla wadai da dakatar da Sanata Natasha.