Wasu da ake zargin ‘yan bindiga da ake kira ‘yan ta’adda na Lakurawa sun kai hare-hare a kan kauyuka biyar, da ke yankin ƙaramar hukumar Arewa a Jihar Kebbi, in da suka kashe akalla mutum 10 tare da jikkata wasu da dama.
Majiyoyin sirri sun shaida wa Zagazola Makama cewa kauyukan da harin ya shafa sun haɗa da Birnin Debi, Garin Nagoro, Yar Goru, Dan Marke, da Tambo.
‘Yan ta’addan sun dira kauyukkan da misalin karfe 8:48 na yamma a ranar 9 ga watan Maris 2025, in da suka banka wa gidaje wuta tare da harbin kan mai uwa dawabi. Daya daga cikin waɗanda suka rasu shi ne Garba Maigari mai shekaru 50, yayin da ba a tantance sunayen sauran mutum tara da suka mutu ba.
An kai wasu daga cikin waɗanda suka jikkata zuwa Asibitin Tarayya ta Birnin Kebbi domin samun kulawar likita, yayin da aka ajiye gawarwakin mamatan domin tantancewa.
A martani ga harin, dakarun sojojin Najeriya, ‘yan sanda, da ‘yan banga sun isa yankunan da abin ya shafa, kuma rahotanni sun nuna cewa zaman lafiya ya dawo a yankin.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Gwamantin Edo ta rushe gidan wani mutum saboda zarginsa da hannu a ayyukan garkuwa da mutane.
-
Gwamantin Kano ta ƙulla yarjejeniyar samar da sabbin motocin sufuri na zamani masu amfani da CNG.
-
Jam’iyyar PDP ta yi Alla wadai da dakatar da Sanata Natasha.
-
Kswanaki biyu bayan rasa ran wasu mutum 16 a wani hatsarin mota a Abeokuta wasu ukun sun sake rasuwa in da wasu suka jikkata.
-
Rundunar sojin saman Najeriya ta sha alwashin ci gaba da kare rayukan al’umma jihar Zamfara.