Daga Suleman Ibrahim Modibbo
Wasu rahotanni daga jamhuriyar Nijar na rundunar sojin ƙasar sun yi nasarar kashe ‘yan bindiga sama da 60 da kuma ƙwato shanu 250 da ‘yan bindigar suka sace.
BBC ta rawaito cewa, sojojin sun samu wannan nasara ne a wani aiki da suka aiwatar na haɗin-gwiwa a jihar Tillabery da kuma taimaka wa manoman yankin gudanar da ayyukansu cikin tsaro a gonaki.
Bello Turji Ya Ƙarya Iƙrarin Kama Ɓaleri Da Sojojin Nijar Suka Yi.
Takunkumai: Wasu Ƴan Nijar Da Najeriya Sun Yi Zaman Dirshen A Ofishin ECOWAS da ke Nijar.
Dakarun dai na samun nasara a kan ƴanbindigar da ke addabar al’ummar ƙasar kamar yadda maƙwabciyar ƙasar Najeriya ke samun irin wannan nasara ta kamawa da kashe gomman ƴanbindigar.
Jamhuriyar Nijar dai ta jima ta na fama da ƴan bindiga da kuma masu ikirarin jihadi a sassan ƙasar, abin da ya haifar da rasa rayukan da dama, da jikkata da asarar dukiyoyi, duk da ƙoƙarin da hukumomin ƙasar ke cewa na yi na kawo ƙarshen matsalar
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Za Mu Yi Ƙoƙarin Rage Kuɗin Aikin Hajjin Bana – NAHCON.
-
CEFTPI reveals best Nigerian Govt agency in transparency, integrity
-
Gwamnatin Tarayya ba za ta saka tallafi a kuɗin aikin Hajjin 2025 ba,-NAHCON.
-
Ƙungiyar Hezbollah Ta Harba Rokoki Kan Runbun Jiyar Makaman Isra’ila A Tsakar Daren Jiya.
-
Babban Sifeton Ƴansanda Ya Umarci Jami’ansa Su Janye Daga Sakatariyar Ƙananan Hukumomin Jihar Rivers.