Tsohon ɗan wasan gaba na Ingila John Fashanu, ya kai ƙarar Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya yana neman diyya ta yiro £100,000 bayan da aka kama shi bisa wasu zarge-zarge daban-daban.
Ana zargin Fashanu da laifuka kamar haɗa baki don aikata laifi, barazana ga rayuwa, tsoratarwa, da kuma kutse.
Sai dai ɗan wasan mai shekaru 62 ya musanta waɗannan zarge-zarge kwata-kwata, yana mai cewa matsalar ta samo asali ne daga gardamar filaye da ke tsakanin sa da wasu masu zuba jari da suka amince su biya fiye da £500,000, domin mallakar filin sa mai girman eka 22.
A cewar jaridar The Mirror, an kama Fashanu ne bayan da ya tambayi wasu yan kwangila da ke gina shinge a filin sa.
Fashanu ya yi ikirarin cewa shi da matar sa Vivian da lauyan su sun fuskanci “kamawa, da tsarewa, da kuma cin zarafi na tsawon kimanin sa’o’i ukku a ranar 16 ga watan Disamba.
Ya kuma zargi ‘yan sanda da take masa hakki, ta hanyar “takura masa a kai a kai” da kuma “sabon wariyar doka da ya ci karo da kundin tsarin mulkin ƙasa.”
Lauyan sa Mista Chigbu, ya tabbatar da cewa: “Dukkan su ukku sun cika sharuddan beli kuma ‘yan sanda sun sake su bisa belin.”
John Fashanu wanda ya buga wa ƙungiyoyin Norwich City, Wimbledon, da Aston Villa, ya kasance gwarzo a ƙungiyar Wimbledon lokacin da suka lashe kofin FA a 1988,kuma ya wakilci Ingila a wasanni biyu na ƙasa da ƙasa.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Ƙudirin dokar da ke neman samar da Ofishin Firainista a matsayin Shugaban Gwamnati a Najeriya ya wuce karatu na 2 a majalisar wakilai.
-
Jami’an tsaro sun kama ɗalibai 59 a jihar Oyo
-
An dawo da ƴan Najeriya kusan 1000 gida daga ƙasar Libiya a farkon 2025 kawai
-
Masarautar Bauchi ta yi amai ta lashe kan soke hawan Sallah.
-
Kwastam ta kwace kuɗi kimanin naira biliyan 289 da aka boyi a katon ɗin yoghurt a Filin Jirgin Saman Abuja