Jami’an Rundunar ‘Yan Sandan Babban Birnin Tarayya Abuja sun hallaka mutane bakwai da ake zargin masu garkuwa da mutane ne, da kuma 9 da ake zargin ‘yan fashi da makami ne a cikin watanni biyu da suka gabata.
Rahotanni sun nuna cewa jami’an ‘yan sanda sun kama mutane dari uku, tare da kwato makamai da harsasai masu yawa, da kuma miyagun kwayoyi daga ranar ɗaya ga watan Janairu zuwa 28 ga watan Fabrairu 2025.
Da yake jawabi kan lamarin, Kwamishinan ‘Yan Sandan babban birnin tarayya CP Olatunji Disu, ya bayyana cewa an tura tawaga ta musamman ne domin kai farmaki a wuraren da ake zargin maboyar masu laifi ne a Abuja.
CP Disu ya ce Dei-Dei, Karu, Gwarinpa, Jikwoyi, Karimo, da Maitama na daga cikin wuraren da aka kaddamar da farmakin.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
An banka wa gidaje 24 da runbunan ajiyar hatsi wuta a jihar Jigawa bayan wani rikici ya ɓarke tsakanin Hausawa da Fulani.
-
Sojoji sun isa wasu ƙauyuka biyar a jihar Kebbi dan farwa Lakurawa, bayan sun kai harin da ya yi ajalin mutum 10.
-
Gwamantin Edo ta rushe gidan wani mutum saboda zarginsa da hannu a ayyukan garkuwa da mutane.
-
Gwamantin Kano ta ƙulla yarjejeniyar samar da sabbin motocin sufuri na zamani masu amfani da CNG.
-
Jam’iyyar PDP ta yi Alla wadai da dakatar da Sanata Natasha.