Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Nasarawa ta kama wani mamba na kungiyar fashi da makami da ke aikata laifuka sanye da kakin soja, a kan titin Abuja zuwa Keffi da wasu yankuna na Babban Birnin Tarayya Abuja.
Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar SP Ramhan Nansel, ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Lahadi a Lafia, in da ya ce jami’an ‘yan sanda daga ofishin Angwan Lambu da ke Keffi, sune suka cafke wanda ake zargin bayan samun sahihan bayanai na sirri.
Ya ce wanda ake zargin mai suna Godswill Achili, an kama shi ne ya na sanye da kakin soja.
Bayanin ya nuna cewa “Bayan bincike, ya amsa da cewa ya na aikata fashi da makami in da ya ke kwaikwayon soja.”
Bincike ya nuna cewa Achili mamba ne na wata kungiyar masu aikata laifuka, da ke fashi da makami a yankunan babban birnin tarayya Abuja da kuma Nasarawa” in ji shi.
Mambobin ƙungiyar na sanya cikakken kakin soja yayin aikata laifukka, suna amfani da bakar mota kirar Toyota Avalon, suna mayar da hankalin su ga matasa da ɗalibbai da ke tafiya tsakanin Keffi, New Karu, da kuma Abuja.
Suna yaudarar mutane su shiga motar su, sannan su kwace musu kayayyaki kamar kudi da wayoyi.
SP Nansel ya ƙara da cewa akwai wasu mutum biyu na kungiyar da suka gudu, kuma rundunar ‘yan sanda tana kan kokarin kamo su.
“Kwamishinan ‘Yan Sanda na Jihar Nasarawa CP Shetima Jauro Mohammed, ya bukaci jama’a da su kasance masu lura tare da kai rahoton duk wata bakuwar ijiya dake nuna alamun aikata laifi don dakile miyagun ayukka a jihar,” in ji Kakakin Rundunar.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Sojoji sun isa wasu ƙauyuka biyar a jihar Kebbi dan farwa Lakurawa, bayan sun kai harin da ya yi ajalin mutum 10.
-
Gwamantin Edo ta rushe gidan wani mutum saboda zarginsa da hannu a ayyukan garkuwa da mutane.
-
Gwamantin Kano ta ƙulla yarjejeniyar samar da sabbin motocin sufuri na zamani masu amfani da CNG.
-
Jam’iyyar PDP ta yi Alla wadai da dakatar da Sanata Natasha.
-
Kswanaki biyu bayan rasa ran wasu mutum 16 a wani hatsarin mota a Abeokuta wasu ukun sun sake rasuwa in da wasu suka jikkata.