Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Zamfara ta mika takardun ceki na kudi har N94,555,327.69, ga iyalan jami’an ‘yan sanda 23 da suka rasu yayin gudanar da ayyukan su.
Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar Muhammad Shehu Dalijan, shine ya mika chekin a madadin Sufeto Janar na ‘Yan Sanda Kayode Egbetokun, a wajen wani biki da aka gudanar a Gusau.
Ya bayyana cewa ko da yake kudin ba zai iya maye gurbin ‘yan uwan su da suka rasu ba, an bayar da shi ne domin tallafa masu a wannan lokaci mai wahala. Haka kuma, ya shawarce su da su yi amfani da kudin ta hanyoyin da za su amfanar da su a nan gaba.
Daya daga cikin wadanda suka amfana da tallafin ya nuna godiya ga shugabancin ‘yan sanda bisa wannan taimako, tare da yin addu’a domin kariya ga dukkan jami’an ‘yan sanda.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
An banka wa gidaje 24 da runbunan ajiyar hatsi wuta a jihar Jigawa bayan wani rikici ya ɓarke tsakanin Hausawa da Fulani.
-
Sojoji sun isa wasu ƙauyuka biyar a jihar Kebbi dan farwa Lakurawa, bayan sun kai harin da ya yi ajalin mutum 10.
-
Gwamantin Edo ta rushe gidan wani mutum saboda zarginsa da hannu a ayyukan garkuwa da mutane.
-
Gwamantin Kano ta ƙulla yarjejeniyar samar da sabbin motocin sufuri na zamani masu amfani da CNG.
-
Jam’iyyar PDP ta yi Alla wadai da dakatar da Sanata Natasha.