Gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara, ya tabbatar wa al’ummar jihar cewa gwamnatinsa za ta yi aiki da hukuncin kotun ƙolin ƙasar, bayan ta yi cikakken nazarin takardun hukuncin.
BBC ta rawaito, yayin wani jawabi da ya gabatar wa ƴan jihar a ranar Lahadi, Mista Fubara ya ce gwamnatinsa za ta bai wa hukumar zaɓen jihar haɗin kai wajen sake shirya wani zaɓen ƙananan hukumomin, bayan kotun ta rushe wanda aka yi a shekarar da ta gabata
A ranar Juma’a kotun ƙolin ƙasar ta rushe zaɓen shugabannin ƙananan hukumomin jihar da aka gudanar ranar 5 ga watan Oktoban 2024.
Gwamnan ya kuma umarci duka shugabbanin ƙananan hukumomin su miƙa ragamar gudanar da ƙananan hukumomin ga daraktocin mulki na ƙananan hukukomin a gobe Litinin 3 ga wata.
Ya kuma bayayna aniyar naɗa shugabannin riƙo har zuwa lokacin da za a sake gudanar da wani sabon zaɓen.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
An banka wa gidaje 24 da runbunan ajiyar hatsi wuta a jihar Jigawa bayan wani rikici ya ɓarke tsakanin Hausawa da Fulani.
-
Sojoji sun isa wasu ƙauyuka biyar a jihar Kebbi dan farwa Lakurawa, bayan sun kai harin da ya yi ajalin mutum 10.
-
Gwamantin Edo ta rushe gidan wani mutum saboda zarginsa da hannu a ayyukan garkuwa da mutane.
-
Gwamantin Kano ta ƙulla yarjejeniyar samar da sabbin motocin sufuri na zamani masu amfani da CNG.
-
Jam’iyyar PDP ta yi Alla wadai da dakatar da Sanata Natasha.