October 16, 2024

Warning: sprintf(): Too few arguments in /home/martabaf/public_html/wp-content/themes/elegant-magazine/lib/breadcrumbs/breadcrumbs.php on line 254

Za Mu Ɗauki Matakin Da Ya Dace Kan Isra’ila Ta Ƙarfin Tuwo.-Khamene.

Jagoran addinin Iran Ayatollah Ali Khamenei ya yaba da hare-haren da Iran ta ƙaddamar kan Isra’ila ranar Talata, inda ya kira su da cewa hare-hare da ke kan ‘ƙa’ida”.

Yayin da yake gabatar da huɗumar Juma’a a birnin Tehran, Mista Khamenei ya ce abin da suka yi ”ɗan ƙaramin hukunci” ne kan Isra’ila saboda ”laifukan ban mamaki da take aikatawa”

Ya kira Isra’ila da mulkin “masu shan jini” da Amurka a matsayin “mahaukacin kare” a yankin.

Mista Khamenei – wanda ke gabatar da huɗubar Juma’arsa ta farko cikin kusan shekara biyar – ya ce Jamhuriyar Musulunci za ta ɗauki ”matakin da ya dace” kan Isra’ila da ”ƙarfin tuwo”.

Isra’ila Ta Ce Za Ta Ci Gaba Da Kai Hare-hare A Gaza.

A Safiyar Juma’ar An Kashe Mutum 109 A Gaza Bayan Ƙarewar Wa’adin Tsagaita Wuta.

Ana Ci Gaba Da Shiga Da Gawarwaki Asibitin Gaza Bayan An Binne Gawa 179 A Cikin Sa.

Ya jaddada cewa Iran ba za ta lamunci ”sassauci” ko ”ɗaga ƙafa” kan Isra’ila ba.

Ayatollah Khamenei wanda ya yi jawabin nasa a harshen Farsi ya jaddada cewa “haɗin kan” Musulmin duniya bisa tafarkin Alƙur’ani shi ne abin da ya zamanto wajibi a tsakanin Musulmi.

“Maƙiyan Iran su ne dai maƙiyan Falasɗinawa da Lebanon da sauran ƙasashen Musulmin duniya.” In ji Khamenei.

BBC Hausa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *