A jiya Asabar ne runduna ta daya ta sojojin Najeriya, reshen Kaduna, ta gudanar da bikin dokin ta na aiki mai suna Dalet Akawala mai muƙamin Sajan, wanda ya mutu a ranar 24 ga Janairu, 2025.
Jaridar Punch ta rawaito cewa bikin binniyar ya gudana ne a hedikwatar rundunar da ke garin Kawo a Kaduna, inda mataimakin shugaban ma’aikata, Kanar I.A Akabike ya jagoranta.
Akabike ya wakilci babban kwamandan runduna ta daya ta sojojin Najeriya da kuma kwamandan sashe na 1 na ‘Operation Fansan Yamma’, Manjo Janar Mayirenso Saraso.
A jawabinsa, Akabike ya jinjina wa marigayi dokin, inda ya bayyana shi a matsayin wani muhimmin bangare na al’adu tarihin rundunar a wannan yanki.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Ɓarawo ya mutu yayin da ya ke ƙoƙarin sata a cikin Taransifoma.
-
Yansadan jihar Adamawa sun fara bincike kan wasu mutum 2 da zargin sun yi wa yara mata biyu Fyade.
-
Yayin da Ƴansandan Kano su ka gargaɗi al’umma kan shiga cunkoso saboda barazanar tsaro gwamnatin jihar ta ce taron Mauludin Shehu Inyass ya na nan daram.
-
Wata gobarar tankar fetur ta ƙone direbanta a Ibadan.
-
Gwamnatin Sokoto ta gargaɗi al’umma kan kwararar ƴan bindiga jihar.