Daga Fatima Suleiman Shu’aibu
Ma’aikatan rarraba wutar lantarki ta jihar Kaduna da ke Arewacin Najeriya ta yanke wa jami’ar ABU Zariya, wuta saboda ƙasa biyan kuɗin wuta da makarantar ta yi.
Cikin wata sanarwa da hukumar jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya ta fitar, ta bayyana cewa ma’aikatan lantarki ta jihar Kaduna sun katse layin lantarkin da ya kai wa jami’ar wuta.
Sanarwar ta ce hakan na zuwa ne bayan gaza cimma matsaya akan kuɗin wutar da jami’ar ke sha a kowane wata, duk da cewa jami’ar ta yi iƙirarin biyan kuɗin wuta na sama da Naira biliyan ɗaya a wannan shekarar.
ASUU ta nuna damuwa kan yawaitar ɗaliban da ke samun sakamakon first-class a Najeriya.
Sama da ɗalibai dubu 12 ne suka zana jarrabawar neman shiga Jami’ar Yusuf Maitama da ke Kano.
NAHCON ta ce kowanne alhajin 2023 za a mayar masa da naira 60,080.
A baya-bayan nan ne dai aka bayyana Jami’ar ABU a matsayin jami’ar da ta fi kowace jami’ar gwamnati fice a Najeriya.
LABARAI MASU ALA'KA DA JUNA
-
Ƴansandan Najeriya Najeriya sun cafke mutum biyu kan rikicin baya-bayan nan da ya afku a jihar Filato
-
Shugaba Tinubu ya ƙaddamar da sabon kwamitin ƙidaya
-
Ƴansandan Najeriya sun ƙi karɓar cin hancin naira miliyan 1 jihar Katsina sun kuma cafke waɗanda ake zargin
-
Me ya sa ƴan Majalisar Wakilai su ka gayyaci Gwamnan riƙon ƙwarya na jihar Rivers?
-
Abin da ya sa Matatar Dangote rage farashin Man Fetur